Tuesday, March 27, 2007

Wakar Zambon Kazama; Aliyu Namangi Zaria

Ya Allahu Rabbana taimakemu
Mu gargadi yan'uwa ga auren kazama

Auren tsohuwa hasara ga yaro
Gwammaci tsohuwa ga auren kazama

In baka san tane ba kau tambaye ni
In Allah ya yarda kasan kazama

Mummunan halin kazama na fari
Bata fece majina sai da dama

Mai son cin tuwonta sai yaci gashi
Susan hagu na tofi da dama

Hanci majina, idanunta kwantsa
Dattsa ya dadawa bakinta girma

Sai kaga tai gajal da suma da dauda
Ga bauli a kwance, tashinta fama

Bamai son kitso ba, ta kasa aski
Taba ya dafe hakoran kazama

Gude ba kokari ba ga kasa girki
Ga hadama a zuci koshinki fama

Ran girki ba a koshi da jibi
Shi naman miji ki cinye a tsama

In taga ka fito kamar zaka zaure
Sai sababi ya tashi don bata girma

Ka ji "Bar neman fita ina tsame nama
Yau dai kai rabon a zage ka kai ma"

Tunda ka sai kitse ya narke a girki
In aka zo rabo, rabawansa fama.

Wanda ka bashi kankane sai ya raina
Kowa so yake ya karba da dama

Ran nan ma ka sai kashi, na ki zagi
Gun kwarin gidanka mai yada girma

In ta ce dani kazama in rama
Wanda ya san Kumatu yasan kazama

In tace ina da ci ne in rama
"Domin ga Tasallah koshinta fama"

Kwana goma jere, haifanta goma
Ba taran miji ga haifan kazama

Ita ko Bante ta ketara sai ta haifu
In ka san kudi su kare a suna

Ya Allah dadawa matanmu tsabta
Kada Allah ka bamu mata kazama

Tunda mijin kazamiya zai ji kunya
Can Aljanna babu mata kazama.

Wakar Keke; Ta [Dr] Aliyu Namangi

Muna shukura ga Rabbal alamina
Da alherin da yai mana ba kadan ba

Muna murna da mulkin ingilishi
Zuwan da sukai kasarmu ba tai tsiya ba

Zama zamaninsu ne aka zo da Faifa
kudi ba masu nauyaya aljihu ba

Dada zarafinsu ne aka zo da jirgi
Kaje Makka ba da tashin Hankali ba

Sa'annan gasu Babur, ga su Mota
Da farko da can bamu san da su ba

Izan tafiya ta faru ka nemi mota
Izan jirgi ba kui daidai da shi ba

Izan kuwa babu Jirgi babu mota
Ka je da kafarka ba keken tsiya ba

Banni da Basukar Ho! Dan jidali
shakiyyi ba abin Babba ya hau ba

A Dan-Mahawayi nih Hau sai ya barni
Tudun-Yakaji ban kawo gari ba

Ya bar ni da jin jiki da zama a turba
Da dai ko juma'a ba a je dani ba

Kudi tirmis! Na bashi Sule-da-Sisi
keke bai mani rangwame ko dari ba

Na ce masa "Basukur rika sawwakewa"
Yace "Malam hala ba ka sanni ne ba"

"Ina da tsiya biyar farkonsu fanca
Na kau buga bindiga ba mai wuta ba"

In babbake zuciya, in tafi da sawu
Cikin daji kamar ba'a je dani ba

Muna tafiya kuma na fizge kaina
Mu fada kwazazzabo ni ban kula ba

Ina da ciki ana ce mai Kurumbo
Karambanin hawa baka saya ba

Hanjina kaca mai kama riga
In fizgo mai hawa ni ban kula ba

Tsiya na can mu je kan kadarko
Madaidaici in ce ba zamu hau ba

In hau bisa kafadar bari in zauna
Kamar mahayin dadai bai hauni shi ba

Su kai kadda da Sale akan kadarko
Sai yace "Haba Sale bazan yadda kai ba"

Dadai suka wantsala hakan kan ya kwace
Ashe ba Sale ne a cikin ruwa ba?

Ya bishi ya bangaje ya buge yana ce
"Azo a gani idan ban yada kai ba"

Malam Sale saida ya tube riga
Yasa kaga Sale har bai sha ruwa ba

ya tashi ya hau tudu keke ya bi shi
Da rigar Sale keke bai sako ba

Su malam Sanda duk suka tar ma keke
Da ban magana yace ba zai saka ba

Ya ma rantse da jirgi har da mota
Ba zashi sako ba in ba'a sa wuka ba

Malam Sanda wai sun shirya da Keke
Wai yana kaunarsa ba domin tsiya ba

Yace "Haba malami kamarka
Bazan iya yadda babban malami ba"

Izan dai zaka hauni ka tara riga
Da wando ba ka hau ni hawan isa ba

Ya tashi hawa bai tattara ba
Ya fizgo malamin ba a jinjima ba

Ya yasai nan da nan a tsakar gidansa
Cikin matansa tun ba a kai dabe ba

Yace "Bari nai kure yashe ka malam
Dama ban kai ka bakin kasuwa ba

Bana son na yada mutum na kirki
Izan ba inda za ai dariya ba

Da motsa kararrawarka da kama burki
Ba zasu hana ni in jefar da kai ba

Yace masa "Bana kara hawanka keke"
Yace masa "ko adankiya ban kula ba"

Hawan da rashin hawan a gareni dai ne
Ban ga abinda zai cutar dani ba

Kamar tafiya ta sauri ko ta fizge
Baka je inda kaso nan da nan ba

Izan kazo ka hau ni ka bani iska
Na sha, ba inda ba zan je dakai ba

Ashe ba mai hawa keke ya more
Izan ba wanda ya iya zanzaro ba.

Monday, March 26, 2007

Wakar Yabon Aikin Lebura; Lawan Maiturare

Fatara mai sa a lalace
Ta ki yarda ma kasan rance
Yinwa mai kai maza kwance
Ta kashe ba sai da aibi ba

Yau Lebura ne kamar Zakka
Aiki rani zuwa kaka
In gwamnati zata sa doka
Lebura baza su karya ba

Aiki kullum cikin taro
Ana abu sai kace horo
In dai Allah ake tsoro
Da lebura bai talauci ba

Bamu san haka zaku fara ba
Kuyi alkawari ku karya ba
Kaya ba za shi zango ba
Lebura bai bada iko ba

Jirgin sama fankamin wofi
Mota bata zuwa rafi
Ta nutsa ta haya ana tafi
Wannan bamu fara samu ba

A hake titi a sa kwalta
Mai mota yai gare keta
Wani Lebura bai da ko mota
Amma bazai ji ciwo ba

Da mun kare ace sauka
Ayi ma ham don a ruda ka
In ka ki gudu a take ka
Ko yau ba za'a canja ba

A dauki diga a wurgata
Kan tsandauri a sara ta
A tara kasa a kwashe ta
Mota ba zata huta ba

Wannan magana ku duba ta
Aiki kullum kamar bauta
In lebura su ake cuta
Allah sa baza su tabe ba

Kai gidan kwano kana yanga
Ai lebura in yasa targa
Kowa ya fito ya zazzaga
Ya dade bai hangi kwanon ba

Ga katako a jejjera
Shima kwanon a tattara
A bar ka dashi ace dora
Mun san ba zaka dora ba

Dubi tara gyada kamar Dala
Kauye da cikin Kano Jalla
A daura guda kamar hula
Amma ba zata goce ba

Kaji nauyin goro huhun nan
Daya ko daukar guda sannan
Ga wagunu fankamemen nan
Lebura ba za su kasa ba

shin Lebura ko waliyyi ne
Ko jikin da ice da karfe ne
Ko dan lada suke yi ne
Ba don karfen bature ba

Icen tunba a sare shi
Ai katako a tsage shi
Wane ne zasu tsage shi
Kan lebura baiyi aiki ba

Ai lebura sai a gode ma
A tara kudi a mika ma
In ba don kai ba tun da ma
Aiki ba zai yi kirki ba

Jirgi da muke gani babba
Ba za ya zuba ya dauka ba
in lebura baiyi lodi ba
Kaya ba za shi zango ba

Ran nan da na dauki mota ta
Muka je yashi ya kama ta
Da lebura sunki tura ta
Don ni ba zata motsa ba

Jirgin ruwa in yazo kwata
Da lebura za su sa keta
Suki yin aiki su kwankwanta
Shi ba zai je ya sauke ba

Tun sanda muke zuwa kanti
Da lebura dan dako Mati
Wani mummuna gwanin datti
Amma ba'a fishi aiki ba

Ai mai amalanke jigo ne
Babban kura ko gwamna ne
Mutum ko shi minista ne
Bazai iya raina lebo ba

In za'a daka asan gari
Daukar kaya ana zari
Kaga lebura har yana tari
Amma bai fasa aiki ba

Du lebura yan kasa ne ku
Ni banda nufin in raina ku
ku amince min cikin ranku
Da nufin ba zamu saba ba

Nan zamu tsaya mu saurara
In lebura su ake kwara
Zamani zai yi wo kora
kowa ba za ya tsere ba

Kai lebura me ya dame ka
Ga Lawan ya zo ya nuna ka
Da nufin a fahimci aikinka
Amma ba don a raina ba

Kullum aka samu mai sona
Zai wo sako zuwa guna
kulkul acikin Kano tona
Lungu nake ba a titi ba

Kowa ya karanta waka ta
Sha Takwas muka tsara baitinta
Don lebura mun ka tsara ta
Amma ba don minista ba

Gaskiya Bata Sake Gashi; M Mu'azu Hadejia

Tarihin Malam Mu'azu Hadejia, dan takaitacce ne. Ya rasu yana da Shekara 38, domin acikin 1958 ya rasu. an haifi Malam Mu'azu Hadeja a garin Hadeja, cikin 1920. shine Bahaushe na farko da ya fara rubuta Wakokinsa da rubutun Boko. Wannan kuwa ya faru ne, saboda acikin marubuta mawakan Hausa, shine wanda ya fara samun cikakken illimin boko. Dangidan Sarautar Hadejia ne, shine dalilin da wakokinsa suka fi maida himma wajen yada aqidun NPC a madadin NEPU. Kila wannanne ya janyo takaddama tsakaninsa da Malam Mudi Spikin. Bayan kammala karatunsa ne, ya fara aikin koyarwa a birnin Kano, har kuma ya rasu aikin da yake yi kenan.
Nayi ta kokarin in san ko yabar baya, amma har yanzu ban samu abin kamawa ba. Na kuma yi kokarin in san ko yana da iyali a birnin Kano, shima dai ban samu abin kamawa ba. Sai dai naji Shata na yiwa Inuwa Mai mai Kirari da "Baban Mu'azu, wanne Mu'azu? Mu azun Hadeja. Haji Inuwa Baban Yahaya" Na kuwa so hakanne don ko zan sami wasu wakokinsa da ba'a buga ba. Naji ya kan yiwa kansa kirari da "V T maineman albarka". Ga dai wata wakarsa, kafinmu kawo muku wasu.

Bin Allah shine babban bi
Kuma sai kabi wanda ya haife ka

Ka kiyaye hududulLahi suna
nan amru da nahyu suna kanka

Wallahi Uwa da Uba sune
Hanyarka ta neman albarka

In sun gajiya bisa zamani
Sai ka dau wahalarsu da karfinka

Yi fata kadda ka sabe su
Wata rana Allah zai saka

Abinda ka shuka don ka sani
Shine ka tsirowa gonarka

In hairi, hairi zaka gani
In sharri, sharri zai bi ka

Wa adi'ulLahu fadar Allah
Kuma girmama wanda ya girme ka

Duk wanda ya raina fadar Allah
Shi ya bata ya auka halaka

Duk wanda ya raina fadar Allah
Shine muka cewa Dan Iska

Har shina wa kansa kirari, sau
rara kaji taken dan iska

Dan iska sandan Kuka da sun
gumi nai ba;a yin taki

Dusar buntu ba'a ba dabba
To kaji kirarin dan iska

Dan iska naman Balbela
Ba a cin shi da na Hankaka

Kilishin Jaba sai dan iska
Ba mai ci sai ko mai shirka

Kashin Bera baya taki
Balle kayi dokin ga-na-ka

Kiwon Yimka, kiwon banza
Wata ran zai gallabi yayanka

Ajiyar Bera ajiyar wofi
Bari murna sabon dan iska

Ni zan hore ka abokina
Bari jawo dan iska ajika

In har ka yarda ya rabe ka
Ba'alin jama'a sa tsarge ka

Zai koya ma mugun hali
Watakil a kira ka da dan iska

Da 'wa kullu karinin' duba man
Ta'alimi ka samu zancenka

Kuma ka zama Shaidanil insi
Sai hirzi kai da masoyanka

Kuma ka zama Fattani domin
Allah ma bai son ka

Ka girmama Allah da Ma'aiki
Da iyaye duk da sarakinka

Wa ulul amri minkum duba
Ka kiyaye fadar mahaliccinka

In ka rainawa sarakinka
Ka rainawa mahaliccinka

Bari jin kyashin baiwar Allah
Mai kaskantawa da daukaka

Shi yadda ya so haka nan zai yi
Da yayi su sarakai, kai talaka

Da yaso zai baka duniya
Ba komai ce ba ga Rabbaka

In yaso sai kaga ka gajiya
Har ka gaza amfanin kan ka

Kai dai riki aikin alheri
Kowa kaya nasa zai dauka

Shine sarki mai fifiko
Da kasanka, wadansu ko sun fi ka

Wani na da Jaka zambar Goma
Wani bashi Kwabo balle fataka

Wani kullum mota za shi shiga
Wani kullum kaya zai dauka

Da tuwon Baure da gudun kurna
Wainar shinkafa Annafaka

Ga Alkaki duk da Alkubus
Allah ya baiwa wadansu haka

Wani sai shi tsugunna kan titi
In anci a miko mai sadaka

Wani mata nai hudu ne, kuma ga
Soraye, Benaye, Taska

shimfidu, da kujeru, Darduma
ko ina sai kamshi ke binka

Sai fenti zane iri-iri
Ga lantarki, kuma ga fanka

Wani bin Zaure shi kayi domin
Wani kasuwa zai je shi faka

Suturar wani ganye ko walki
Ba rigarma balle shi saka

Shi kance daurin Allah,
Ya daure bawa nai a daka

Wani ga sutura nan iri da iri
Ya jibge wasu cikin adaka

Kullum sai ya sake tsari
Duk wadda yaso ita za shi saka

A gidan wani guda zaka ji don
A gidan wani kuka za'a saka

Kai ba'awa Allah tilas
Shi yadda yaso haka zai baka

Da abin dariya dana mamaki
Ba sa karewa ba shakka

Wai kura ce aka ce ta tu
ba da sata don tsoron halaka

Makiyayi sai amince har
Ya kafa mata turke cikin maruka

Shi mai hakuri shike dafa du
tse ya sha romo mai albarka

Ya Allah taimaki bayinka
Duk wanda yake son manzonka

Mu'azu Hadejia nan ya tsaya
V T mai neman albarka

Batijjaniya; Daga Alu Dansidi Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau Alu dan Sidi, shine sarkin Zazzau na farko da turawa suka fara nadawa, bayan sun ci kasar Zazzau. Ya mulki kasar Zazzau, tun daga 1903 zuwa 1922. Ya samu matsala da turawa, domin banbancin ra'ayi, wanda hakan ya sanya suka cire shi. Fasihin marubucin wakoki ne, kuma zamu kawo muku wakokinsa da dama. Da yake cikakken Batijjane ne, wato mabiyin darikar Tijjaniya, shi yasa muka fara da wakarsa ta Shehi Ahmadu Tijjani.

Na sha ruwan bege dada ni bani ji
Da gani ba, sai na zo gurin Tijjani

In na fito can zani nan in dawayo
Ni zani birnin Fas wurin Tijjani

kai mai zuwa Fas dakata mani zani nan
In yo ziyarar Ahmadu Tijjani

Shehunmu Ahmadu anka ba al-Fatihi
Budi Lima ughliqa sai Tijjani

shi anka ba al-Khatimi ga lima Sabaqa
Kuma Nasirul Haqqinmu sai Tijjani

Bil haqqi wal hadi kasan shi anka ba
Wa ila siratul mustaqim Tijjani

Wabi alihi ya Rabbi haqqa li Qadarihi
Miqdarihi ya al'Azim Tijjani

Sabkakkiya take inda Rabbil Izzati
Ita anka saukowa Wali Tijjani

Domin wadanda su kai shahada ran Badar
Don Makka duk da Madina don Tijjani

Ya Rabbi don Taurata har Injilu duk
Da Zabura har Furqanu don Tijjani

Domin safa don Marwa don Hajaral lazi
Sunansa Arfa, Rabbu don Tijjani

Domin Badiha Rabbu domin Zamzamu
Da Mukamar Ibrahimu don Tijjani

don hajaral Aswadu wanda kaba alkawal
Ran tambaya kalubale Tijjani

Yabon Allah; Daga Wazirin Gwandu Umaru Nasarawa

Malam Umaru Nasarawa dai ba boyayye bane, domin a zamaninsa kowa yasan irin gudunmawar da ya bayar wajen raya adabin Hausa ta fannin wakoki. Ya rubuta wakoki da dama, wanda insha Allah zamu kawo su. Amma ga wanda bai san shi ba, to shine mahaifin tsohon gwamnan jihar Kaduna a zamanin soja, wato; Abubakar Dangiwa Umar. Wannan wakar dai sunanta Yabon Allah. Ga kuma yadda take.

Yabo gun Jalla daidai na
Garan kuma wajibina na
Na jin kai nai da yan nuna
Garan ya amshi roko na

Tutur! Na zam shukura
Ga sarkin nan da naiyi kira
Da sunayensa naiyi bara
Zuwa ga biyan bukatuna

Da farko duk abinda ni kai
Da fari dai salati ni kai
Ga Annabi duk abinda ni kai
Da shi nika fara wake na

Sahabbai nai da Alu duka
Gama sun taimake shi duka
Ina ko daulaminsu duka
Da aikina da horo na

Abokina taho ka jiya
Ina rokonka kar ka kiya
Ka samu guri guda ka tsaya
Idan ka amshi roko na

Tsaya gun Jalla dai ka fake
Da imaninka kar ka fake
Ka bishi ka togi inda shike
Mu dogara nan masoyi na

Biyar Allahu ta wajaba
Sana'a ta mafi riba
Tutur! Batu na bai da tambaba
Tsaya in baka shaiduna

Ruwa bana sun ka kai ga wuya
Har na rasa inda zani tsaya
Balle juyi, balle tafiya
Ganin am fara zunde na

Rawata an suke ta duka
Gama an dungushe ni haka
Ganin ta kai ni ag ga haka
Dada nir raina wayo na

Dada sai nik kirai Ahadun
Guda, wannan da as-Samadun
Da nim matsu ni nufai da gudun
Gama shi am maceci na

Da nat tasamma inda shike
Cikin huruminsa ni iske
Aminci nan gare shi shike
Dada nid debe tsoro na

Da dai nig gane Sarkina
Da ba a bida garai shi hana
Ga kofofinsa niz zauna
Dada ni buda baki na

Dana roka da ya bani
Dani dauko ga Qur'ani
Ashe ma anyi min izini
In tai in kara koke na

Da najji hakanga nish shirya
Bido Zababbiya ka jiya
Cikinta kana ganin hanya
Da zam bi ta zam mahorina

Taho sa hankali ka kula
Kabar gajiya, kabar shagala
Tutur! mu tsare yabon Allah
Cikin zarafin zamowa na

La'in mun zo ga Qur'ani
Bisa horonka don ka sani
Ina tsaya ran dare da wuni
Ina shukuri da Bege na

Tabara yabonka jalli na
Gareni abin tsimina na
Sahihin maganina na
Da shi nika warke rauni na

Da lotto duk yabonka ni kai
Dana matsu duk kiranka ni kai
Bida bisa agajinka ni kai
Ka warwatse aduwai na

Kana nan inda nis sanka
Tutur! Ka amsa sunanka
Mujibun kow kireka haka
Kana ji baka yin kwana

Da kyau nas soka nab bika
Da kowa baiyi ma shirka
Ilahul Arshi baicinka
Wane ka biyan bukatu na

Ina wani banda kai Rabbu
Da ba a bida shice babu
Ina wani mai kade aibu
Gareni shi karbi rokona

Ku kawo wanda kun ka sani
Da komi za ayi shi sani
Da an roke shi bashi hani
Fada mini shi, ka ban suna

Kace Allahu sarki na
Wani nai dug gazajje na
Abi nai duk kadan dai na
Ina shika jure roko na

Bida ga waninka mik kai ni
Dadai duk wanda yas sanni
Cikin ni'imarka yag ganni
Kana da kula da raino na

Ka cetan kar a kaushe ni
Ga duk hanyar da shaidani
Rajimi kar shi rudeni
Shi hau kan yan dibaru na

Ta'ala kai da ka hora
Mu zan koko mu zan ta bara
Gareka mu zam bidan Nasara
Dashi ni kayo umurni na

Ta'ala Jallah mai iko
Ina nan dai ina dako
Ina ta kiranka kullum ko
Ina kuma kara kwazo na

Da farin na kiraye ka
Da sauri nig ga jinkanka
Ina gode ma baiwarka
Dashi ni ka rera wake na

Ta'ala bani fasa bara
Tutur! Ni ke duk cikin zakara
Ginarka gareka ga sutura
Wadarka, ka kore bakakina

Bukatu na matso ni su kai
Dana matsu ko kiranka ni kai
Tutur! Sonka bani ni kai
Ina nika kama bakina

Bukatu gasu sun gilma
Ilahi gani na soma
Kiran nan wanda nif fara
Da farko nigga dace na

Da farin gafara zambu
Nike roko wurin Rabbu
Da aikina nayin aibu
Da son raina da wayo na

Ka hori ga zuciya ta tsaya
Bida ga waninka duk ta kiya
Balle inyo haraminya
Garai in banna baki na

Isheni ga duk abinda nik kai
Biya min duk bukin da ni kai
Gama kasan nufar da ni kai
Ya Rabbi ka amshi rokona

Sunday, March 25, 2007

Wakar Tsuntsaye; Daga Ahmadu Dan Matawalle

Amshi: Rabe! Ribabe!! Bamu jawabin na Garba mai Yammata

1] Tsuntsayen gida da daji, sun hadu sun girka shawara, Jimina itace gwamna tace zata yi musu Sarki.

2] Agwagwa aka bai sarauta, sunce wofi marar karama, yar banza mai kama da gammo, bata da siffar da zasu bita kazama.

3] Hankaka ka bai sarauta, sun ce su dai ba zasu lamunta ba, sun sake shawara suna cewa 'Danfashi' bazai sarki ba.

4] Aka bai Mikiya sarauta, sunce wannan in ta samu mulki, ita wa zaya ganta, sai ko mushe ya fadi zaka ganta da sauri.

5]Borin-Tunke ka bai sarauta, tsuntsaye duk suna ta mamaki, sai wannan ya dubi wannan, wai dan sun sami Shugaba maigirma.

6] Da Shaho yazo da kansa, tsuntsaye sai suke ta mamaki, sai wannan ya dubi wannan, Shaho yazo shi babu sauran wargi.

7] shaho ta bai sarauta, tsuntsaye sai kuzo ku kai caffa, Borin-Tunke ka dau jakarka a hannu.

8] Fadawa kuzo nadin Shaho, Zabin dake cikin dawa, sune yan figini mabusa Sarki.

9] Zalbe ka baiwa mai Kakaki, yan doka tambura ne Burtu.

10] Zagage ka baiwa Balbela, Zakaran Kekuwa kasa yan kurya

11] Ga Tsintara tana algaita, ga Hasbiya tana buga Jauje

12] shaho yana jawabi, Borin tunke ka bai Waziri, Gauraka ne Ciroma mai alfarma.

13] Kuma Tuje ka bai Galadima, Madakin gari ka baiwa Dinya.

14] Sarkin Bayi Shamuwa ce, sannan Sarkin dawa Kitsawa ce, Alkalin gari ka bai Kahuhu.

15] Marke ka baiwa Yari, Sa'annan angulaye kurhu na banzar gari madeba kashi.

16] Sarautar da zata dace!! Farin Barugu shi ka baiwa limami, sannan na baku labari, kuma sannan Kadafkara shine Ladaninsa ko dare ko rana.

Wanda ya rubuta, shine ".........Sahibul BBikru, sahibul Fatyatu, mai yanmata" Ku bini bashin sharhin.
Muhammad Fatuhu Mustapher

Mulkin Audu; Daga Abdullahi Gwandu

Abdullahi Gwandu, ko kuma Abdullahi bin Fodio, kani ne ga mujaddadi Usman bin Fodio. Masani ne, kuma marubucin wakokine, ya rubuta wakoki da dama, cikinsu harda wannan da zamu gabatar, da kumawakar cin birnin Alkalawa da insha Allahu itama nan gabazamu kawota. Sai dai wasu baitocin sun karye, saboda dadewa, da kumarashin ma'ajiyi nagari. Hakan yasa dole na kirkiri wasu baituka, misali a Baiti na23, 33, da kuma na 40. Ga dai wakar yadda take;

Mai dare duk da safiya
Mai sarauta da gaskiya
Rabbu tsarshe mu ghashiya
Mun yi aiki da sunkuya
Mai sarauta da mallaka
Kad da iko da daukaka
Wanga bawa ka tsarkaka
Nashi haush ga zuciya
Jalla kai munkawakkala
Al'amurranmu duk kala
Don ka fisshe mu Dan'bala
Tunga daki na duniya
Mun sake rai shika hawa
Harzunabbanmu sun yawa
Ga tubanmu yai nawa
Mun yi tsufada ma'asiya
Don nabiyunka mai hima
Mai darajjaga mai sama
Wanda yak kai ta kau sama
Bani afuwa da afiya
Mun sani wallah zamuna
Randa mutuwa tafar mana
Babu shakka ta ram muna
Namu matada dukiya
Kaitammu radda anka ce
Yau ina wane? Ya wuce
Duk abinai a ya gushe
Duk magada su sha miya
Randa ranakka tazzaka
Sai ka mance da da jika
Dukiyan naka kaf faka
Bata fansalka ka jiya
Masu jiya su tunzura
Babu iko ga ko daya
Sai su zauna su sa ido
Maigida ya tsakar gado
Bashi murnar abin ado
An fakai yau da tsintsiya
Sai ladama ga ko ina
Sai kira har su jinjina
sunyi taro na adana
Har su kai inda kats Tsaya
In nagarta da sunkuya
Duk ka shaida su dai daya
Ga Nakiri da Munkari
duk suna kan ka sun tsaya
In Bakwai yayi kaddafu
Kai da tsutsa ka garwaya
Ran kiyama ana kira
Duk mutane mu tattara
Bamu so bamu faskara
Yau hukumci ga mai shiya
Ke kasa koma rariya
Duk amayo su ke jiya
Kad ki bar dai da danmaya
Zasu na yau wurin biya
Yau asiri ka bayyana
Kun taho duk da jingina
Wansu can sunka dangana
An nagirshe su sun kiya
Ga safun jinni su duka
Ga wuta ga mala'iku
sunka saka da mu tsaka
Yau ina masu mallaka
Masu iko ga duniya
Masu karfi da dukiya
Gamu dai sai mu tsaitsaya
Yau sarauta ga mai niya
Ga kasa bata takuwa
Ga mu rana ga kwalluwa
Ga zufa harga dudduge
Har kafafu su zuzzuge
Babu bance bale lage
Babu ko masu dariya
Ayi hukunci a rarraba
Kafiri duk a azzaba
Kaji ranar bugun gaba
Mumini duk wurin zama
Nashi dubashi dawwama
Nan ga sarki madawwama
Jalla mun roki gafara
Tun gabanin shiga sara
Don ka sha she mu kausara
Don nabiyunka mahiya
Bamu ceto na Annabi
Rabbu shashe mu salsabi

Friday, March 23, 2007

Hawainiya - Mal Tijjani Tukur Yola

Tukuici ga Magaji Galadima

****

Idan banda karya rashin kunya
A dakinka jaki ya zage ka?

A ce wai kiyashin cikin rami
A zaga gari yafi Hankaka?

A murya ace Kurkudun daji
Akan Bushiya yafi Gauraka?

Wajen kwarjini wai ace Akuya
Tana dara zaki abar Shakka?

A ce kai mutum duk tunaninka
Biri wai a can dawa yafi ka?

A tashi ace maka dan Babe
Yana zarce tsuntsu kana dauka?

A ce maka danjinjirin mako
Kawai ya tashi ya bika?

A ce gashi Zaki yana ruri
Kawai "Kwa" na Kwado ya kore ka?

Idan banda an raina wayonka
Ta yaya aboki da girmanka?

A ce maka ga wani inhihi
Na jikanka wai shi ya girmeka?

Kawai dan da kaine ka haife shi
Mutane suce shi ya haife ka?

Dila inda ya kai wajen tsiwa
Yana cewa Zaki ina kin Ka?

Ta yaya ace gaka ga Malam
Kace Jahili sai ya kareka?

Kawai dan anace da kai Zaki
Su Karkanda sai su ji tsoronka

Idan banda wauta da shashanci
Ta yaya Tabo zai rike Dirka?

Ta yaya a zafi wajen harbi
Duhu a gama shi da cinnaka?

idan banda dajin akwai duhuwa
Ta yaya Maharbi yake shakka?

Zaman nan da sake a dai duba
Idan babu Taki ana shuka?

Idan ba ruwa rayuwan jama'a
Ina zata je, ko akwai iska?

Idan ba abinci ina Homa?
Idan ba kudi wa yake harka?

Da niyya ka cinna wuta daki
Kace masu fetur su zo gunka?

Idan garwashi an zubar a kasa
Idanunka sun ganshi ka taka?

Idan wani zai baka Rumbunsa
Yana ce da kai ka kashe kanka?

Kawai don gudun kar a zarge ka
Kana kin fita tallafin kanka?

Ganinka batun nan na wasa ne?
Kana kin nasihar masoyinka?

Abin ya wuce hira ko Bilhu
Ka tauna da kai da makwabtanka?

Idan har kilu zata jawo bau!
Su Tijjani kwayar suke dauka?

Ka ringa kula kar ka sha gwaiba
Kawalwalniya kar ta dauke ka?

Aboki idan gaskiya ka rike
Ka lura da duk masu kaunarka?

Saura kuma kwaji daga gareshi, batun ko wa yayi wakar, kuma me yasa aka yi ta. Ni dai dama nayi alkawarin zan kawo ta.

Muhammad Fatuhu Mustapher

Ya Ghiyathul Mustaghithina; Daga 1896

Ya ghiyatha'l-mustaghi thina-
na wa khairil-nasirina
Agaza ni kad ka bar ni
Ga dibarata ta kaina,
Yi dibara mai dibara
Rahmanu kaji kaina
Rabbu duban ni da Rahma
Anta Kharul Rahimina
Rahmakka sabiqata
Jinkanka wabili na
Babu mai yi sai da yinka
Wanga zance haka nan na
Kai kayi ba taliki
Taliki kau ajizi na
Rabbu kai dai aq Qadirun
Jalla sarki qadiruna
Babu sarki daga Allah
Shi fa sarki gaskiya na
Wanda yai sammai da kassai
Wanda yayi dare da rana
Wanda yayi duniya da Barzakh
Ba ta tsar mai ko ina ne
Wanda yai ran alkiyama
Shi azizi na gwanina
Wanda yayi wuta yai al jan-
-na hakika fatiri na
Agaza ni na kiraka
Don Muhammad yo i'ana
Rabbu tsarsan daga sharri
Masu sharri mufsiduna
Masu Hasada da adawa
Da gamani kha'inina... ........

Kai fa kac ce kana haqqan
Fika nasru l muminina
Don Muhammadu ya ilahi 'l
Arshi tsrsan makiyana
Bani Ikon shafe bid'a
Bani ikon raya sunna....... ...

Wannan wani shagube ne da wani marubuci shahararren malami da akayi, a karshen karni na 19 ya rubutawa Sarki musulmi Attahiru, bayan yaki amincewa da yin mubaya'a gareshi. Jika ne ga Danfodio, kuma ya taba ikirarin zama Khalifa Mahdi a Daular Sokoto. Daga baya ya koma ya zama Babban na-hannun-daman Rabi bin Fadhlallah. Daga baya sun bata da shi, inda har ta kaisu ga shata daga, wanda ya zama ajalinsa. Daga baya iyalinsa sun koma Kano da zama. Inda a yanzu suke zaune a Kofar Mata. Ban sani ba, kowani zai iya gano min waye wannan bawan Allah?

Sha'iri Audi Gwandu - Kigon Mawaka

Da yawa basu san wannan bajimin mawakin ba, Audi Gwandu dai jikan Sarkin Gwandu Halilu ne (1833- 58). Amma duk da cewar shi dan sarauta ne, ba'a samu cikakken tarihinsa ba. Amma dai an hakikance shi a zamaninsa mutafannini ne, kuma Arifi. Yayi karatu a hannun Sarkin Tambuwal Umaru Dan Buhari, kuma Sufi ne na kin karawa. Audi yafi sha'awar yawace-yawace, wannan nema yasa ba'a samu mafi yawan ayyukansu da kuma rubuce-rubucensa ba.
Ya fara rubuta wakokinsa tun wajen 1864, kuma ya rayu har zuwa lokacin turawa. Biyu daga cikin wakokinsa da na ci karo dasu, sune wakar da ya rubutawa shahararren jarumin nan wato Garba Jamborodo, sai kuma wata waka da yayi, sai kuma wata waka da yayi a gaban sarki musulmi Ahmadu dan Atiku.

Ance wata rana, sarkin musulmi ya takali Audi da batun waka. Inda ya kalubalance shi da in ya cika sha'iri kuma fasihi, yayi masa waka da baitukanta zasu ringa karewa da "K'O" Ai kuwa nan da nan Audi ya shiga aikinsa. Ga dai kadan daga cikin wakar

Wata safiya gida zaka yita,
Wata ko kayo kana bako.

Wani kai ka bashi, wani ko shi baka
Wani ko tutut, yana roko

Wani ya taho kamat bai taho ba,
Wani na gida ana sako

Wani sai hura ga masakki ya shata
Wani ko yasha ga dan koko

Wani saurayi samaki gare shi
Inya biyo asha Kiko

Wani saurayi kabuli gareshi
Inya biyo ana leko

Wata baibaya ga Bunu ka yo ta
Wata ko ayo da jan Bako.......

Wannan kadanne daga irin gudunmawar Audi Gwandu. Ga mai son yasan wakarsa da ya rubutawa Garba Janborodo, sai ya nemi Kasidar Dr Bello Said, wanda yayi akan tahmisin wakar da Sambo Wali ya rubuta, kuma wacce ya gabatar a Harsunan Nijeriya XIX 2001. CSNL, BUK.